1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mutane kusan 60 sun rasu a Afirka ta Tsakiya

October 9, 2013

Tashe-tashen hankula tsakanin sojojin sa kai da tsoffin 'yan tawayen ƙungiyar Seleka a ƙauyen Gaga na ci gaba da janyo asarar rayuka a ƙasar.

https://p.dw.com/p/19x4q
Troops in charge of disarmement ride through the Cattin neighborhood of Bangui on September 5, 2013. Authorities in the Central African Republic have begun a new disarmament campaign aimed mainly at rebels who overthrew in March 2013 President Francois Bozize, who had ruled since a 2003 coup. Public Security Minister Jose Binoua said on September 4 the campaign is a response to a surge in robberies, auto thefts, rapes and murders blamed largely on fighters with the Seleka rebel movement. The rebels' leader, Michel Djotodia, was sworn in as president last month, but has so far struggled to restore stability. AFP PHOTO / PACOME PABANDJI (Photo credit should read PACOME PABANDJI/AFP/Getty Images)
Hoto: P.Pabandji/AFP/GettyImages

Kimamin mutane 60 aka kashe a rikice-rikicen ƙabilanci tsakanin sojojin sa kai da tsoffin 'yan tawaye a jamhuriyar Afirka ta Tsakiya. Hakan dai na faruwa ne a daidai lokacin da ƙasar Faransa ke matsa ƙaimi da tsoma bakin ƙasashen duniya. Ƙasar mai arzikin ma'adanan ƙarƙashin ƙasa amma ke fama da talauci, ta tsunduma cikin ruɗani tun bayan da 'yan tawayen Seleka akasari Musulmi daga arewacin ƙasar suka kwace iko a birnin Bangui cikin watan Maris bayan sun hamɓarar da shugaba Francois Bozize. Shugaban riƙon kwarya Michel Djotodia ya rusa ƙungiyar 'yan tawayen amma gazawar gwamnatinsa wajen shawo kan rikicin ta sa gwamnatin Faransa kira ga Kwamitin Sulhun Majalisar Ɗinkin Duniya da ya tura dakarun ƙasa da ƙasa don mayar da doka da oda. A ranar Litinin wasu sojojin sa kai sun kai hari a kan wuraren Seleka da ke ƙauyen Gaga inda suka kashe tsoffin 'yan tawaye hudu kafin su kai hari kan Musulmi fararen hula. Su ma mayaƙan Seleka sun mayar da martani a kan Kiristoci da ke kauyen.

Mawallafi: Mohammad Nasiru Awal
Edita: Abdourahmane Hassane