1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Steinmeier: Ci gabanmu na hannunmu

December 25, 2018

Shugaban kasar Jamus Frank-Walter Steinmeier ya yi kira ga 'yan kasar da su maganta matsalolin da ke faruwa lokaci zuwa lokaci a tsakinsu ta hanyar musayar yawu.

https://p.dw.com/p/3AdBm
Bundespräsident Frank-Walter Steinmeier Weihnachtsansprache 2018
Hoto: Reuters/A. Hilse

A sakonsa na musamman albarkacin bikin Kirsimetin bana, Shugaba Frank-Walter Steinmeier ya ce ba zai yiwu kasar ta rabe saboda wata 'yar rashin fahimta ba. 

Shugaba Steinmeier ya ce galibin mutane na fifita abin da suke so ne ta hanyar wofinta duk abin da wasu suka yarda da shi a kullum.

Jamusawa a cewar shugaban kasa ba su yawaita yi wa juna magana ko uzuri, yana mai jaddada cewa dukkanin al'umar kasar mutane daya ne, koda kuwa daga ina suka fito ko yanayin launin fata ko kuma abin da suke ra'ayi.

Bambance-bambancen siyasa ko zamantakewa a Jamus dai sun karu cikin wannan shekarar ta 2018 da ke shirin ban-kwana, inda wasu ke ta nuna fushinsu ta shafukan sada zumunta maimakon zama don warware su cikin girma da arziki.