Muna amfani da "Cookies" domin inganta abubuwan da muke wallafawa a intanet. Za ku iya samun karin bayani a kundin kare bayananmu.
A cikin shirin za a ji cewar shugaban gwamnatin Jamus Angela Markel ta tattauna ta wayar tarho da zababben shugaban Amirka Joe Biden inda ta taya shi murna da kuma jaddada kudirin karfafa hulda tsakanin nahiyar Turai da Amirka.
An shirya shugabannin biyu za su tattauna batun kara ba da makamai ga Ukraine wadanda suka hada da tankokin yaki masu sulke.
Shugaban Amurka Joe Biden ya ce janyewar da Rasha ta yi daga cikin yarjejeniyar kawar da makaman nukiliya ta New Start wani babban kuskure ne.
Kasashen Turai suna kara daura damarar yaki sakamakon kutsen da Rasha ta yi a Ukraine, kamar yadda rahoton cibiyar kula da zaman lafiya ta duniya da ke kasar Sweden ya nunar.
Jamus na ci gaba da zawarcin kwararrun ma'aikata 400,000 a kowace shekara don cike gibin da take da shi a fannin kwadago sakamakon tsufar al'umma. Galibin ma'aikatan da ke shigowa Jamus daga ketare suna sake ficewa.