A cikin shirin za a ji cewa dakarun tsaron Najeriya sun kwace iko da barikin sojan garin Marte da ke yankin Arewa maso gabashin Najeriya, a yayin da sojan Munisca naMajalisar dinkin Duniya a Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya suka karbe iko da garin Bagassou daga hannun 'yan tawaye.