Jamhuriyar Nijar ita ce kasar da ta fi kowacce kasa fadin kasa a yammacin Afirka kuma kashi 80 cikin 100 na kasar Sahara ce.
Faransa ce ta yi wa Nijar mulkin mallaka inda ta samu 'yancin kanta a shekara ta 1960. Yamai shi ne babban birnin kasar. Kididdiga ta nuna cewar Nijar na daya daga cikin kasashe matalauta a duniya.