1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Najeriya: Rikicin gida na Jam'iyyar APC a Niger Delta

Salissou Boukari
August 15, 2018

Wata sabuwar rigima ta barke a Jam'iyyar APC a Jihar Rivers tsakanin bangaren Minista Rotimi Amechi da na Sanata Magnus Abbe bangarori biyu da ke gaba da juna.

https://p.dw.com/p/33Crx
Karikatur: Nigeria APC Streit
Hoto: DW / Abdulkareem Baba Aminu

A halin da ake ciki kamar yadda wakilinmu na yankin Niger Delta Muhammad Bello ya ruwaito mana, an aike da jami'an tsaro domin shawo kan wannan arangama, da ta hada har da harbe harben bindigogi da harba barkonon tsohuwa.

Arangamar da ta faru a babban ofishin jamiyyar na Jiha da ke kan Aba road kusa da Garrison, na zaman arangama ta biyu a cikin mako daya a jihar. Sai dai kokarin wakilin namu na jin ta bakin rundunar 'yan sandan jihar kan wannan batu ya ci tura.