Najeriya: Atiku Abubakar zai wa PDP takara | BATUTUWA | DW | 29.05.2022
  1. Inhalt
  2. Navigation
  3. Weitere Inhalte
  4. Metanavigation
  5. Suche
  6. Choose from 30 Languages

BATUTUWA

Najeriya: Atiku Abubakar zai wa PDP takara

Babbar jam'iyyar adawa a Najeriya PDP, ta zabi tsohon mataimakin shugaban kasar Atiku Abubakar a matsayin wanda zai tsaya mata takarar shugabancin kasa a zaben 2023 da ke tafe.

Najeriya I Atiku Abubakar I Dan Takarar Shugaban Kasa I PDP

Tsohon mataimakin shugaban Najeriya, Atiku Abubakar

Wannan dai na nufin tsohon mataimakin shugaban Najeriyar Atiku Abubakar din, ake fatan ya gaji shugaban kasar mai ci Muhammadu Buhari. Mai shekaru 75 a duniya, Abubakar yasha kaye a hannu Buhari da a yanzu haka yake kammala shekaru takwas a kan karagar mulki lokacin da aka zabe shi a wa'adi na biyu a zaben da ya gabata na shekara ta 2019. Jam'iyyar PDP din dai ta kwashe shekaru 16 tana mulki a Najeriya, kafin jam'iyyaar APC ta Shugaba Buhari ta karbe iko shekaru bakwai din da asuka gabata a yayin zaben shekara ta 2015.

Najeriya | PDP I Zaben Fitar da Gwani I Shugaban Kasa

Atiku ya lashe zaben fitar da gwani a Jam'iyyar PDP mai adawa a Najeriya

Tsohon shugaban majalisar dattawan Najeriya David Mark ne ya bayyana tsohon mataimakin shugaban Najeriyar Atiku Abubakar a matsayin dan takara na jam'iyyar PDP ta adawa a zaben na badi. Abubakar din dai ya samu kuri'u dai-dai har 371 wajen doke abokan takararsa 11 a wata fafatawa mai zafi da ta dauki hankali cikin Najeriyar da ma a wajenta. Gwamnan Rivers Nyesom Wike ne dai yazo na biyu da kuri'u 237 a yayin kuma da Abubakar Bukola Saraki ya zo na uku bayan da ya samu kuri'u 70. Wannan matakin na PDP dai, ya kawo karshen tsarin karba-karba da jam'iyyar ta yi amanna da shi a baya. Sai dai ba duka ne suka yi farin ciki da sakamkon zaben ba, inda magoya bayan gwamnan Rivers Nyesom Wike ke yin korafin da ma sun san za a rina.

 

Sauti da bidiyo akan labarin