1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jamus za ta janye jami'anta na diflomasiyya daga Nijar

March 21, 2026

Jamus ta ce za ta janye dakarunta na jami'anta na diflomasiyya daga Jamhuriyar Nijar na dan wani lokaci sakamakon halin rashin tsaro a kasar da ke yammacin Afirka.

https://p.dw.com/p/5Apzy
Shugaban mulkin sojin Nijar, Abdourahamane Tiani
Shugaban mulkin sojin Nijar, Abdourahamane Tiani Hoto: AFP

A sakon da ta wallafa a shafinta na intanet, ma'aikatar harkokin wajen Jamus ta ce, sakamakon hali na matsalar tsaro za a sauya wa offishin jakadancin Jamus da ke Yammai mazauni zuwa wajen birnin. Jamhuriyar Nijar da ke karkashin mulkin soji a yanzu, ta dade ta na fama da matsalolin kungiyoyin da ke gwagwarmaya da makamai da suke da alaka da Al-Qaeda da kuma IS.

Karin bayani:Nijar: Matsalar tsaro na kamari a yankin Sahel

Ma'aikatar ta Jamus ta ce, 'yan ta'adda sun fi farautar 'yan kasashen waje a kai hare-harensu da kuma yin garkuwa da su. Ko a watan Janairun wannan shekarar, Amurka ma ta bukaci ma'aikatanta da ba sa yin aikin gaggawa da su fice daga Nijar din saboda halin tsaro.