1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jamus: SPD za ta shiga shirin kafa gwamnati

Yusuf Bala Nayaya
December 7, 2017

A cewar Schulz dai dole kasar ta Jamus ta kara samun karfi lamuranta su inganta, wannan shi ne burin da mambobin jam'iyyar ta SPD za su sanya a gabansu.

https://p.dw.com/p/2owIG
Berlin Bundesparteitag der SPD
Hoto: picture alliance/AP Photo/M. Schreiber

Jagoran jam'iyyar Social Democrats (SPD) a nan Jamus ya bayyana a wannan rana ta Alhamis cewa 'ya'yan jam'iyyar sun mara baya a tattaunawar da za a yi da Shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel don kawo karshen kiki-kaka da siyasar kasar ta shiga.

Martin Schulz ya fadawa babban taron na jam'iyyar SPD a birnin Berlin cewa abin da ke da muhimmanci shi ne wace rawa jam'iyyar za ta taka a gwamnati idan aka aje banbanci da ke akwai tsakaninsu da jam'iyyar ta Merkel CDU masu ra'ayin mazan jiya.

A cewar Schulz dai dole kasar ta Jamus ta kara samun karfi lamuranta su inganta wannan shi ne burin jam'iyyar ta SPD.