1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Boko Haram ce ta kai harin Diffa

Abdul-raheem Hassan
December 14, 2020

Kungiyar Boko Haram mai alaka da IS a fafutukar kafa daular musulunci, ta tabbatar dauki alhakin kai harin da ya kashe mutane sama da 20 a wasu kauyuka a jihar Diffa na kasar Nijar.

https://p.dw.com/p/3mhgF
Nigeria Baga | Truck des IS Gruppe (ISWAP)
Hoto: Getty Images/AFP/A. Marte

Cikin wani sakon bidiyo da kungiyar ta fitar, an ga wani dan kungiyar sanye da kakin soja rabin fuskarsa a rufe, inda ya yi ikirarin kai harin da harshen hausa tare da barazanar kai wasu hare-hare a yayin bukukuwan kirsimeti.

Tun shekarar 2009 mayakan Boko Haram suka fara barna a Arewa maso gabashin Najeriya, sama da mutane 36,000 sun mutu yayin da kungiyar ke cigaba da barazana a kasashen Nijar da Kamaru da Chadi duk da alkawarin gwamnatoocin na murkushe tasirin kungiyar.