1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An yi garkuwa da wani Bajamushe a Nijar

Yusuf Bala Nayaya
April 12, 2018

Wani ma'aikacin agaji dan asalin Jamus ya fada hannun masu garkuwa da mutane a Jamhuriyar Nijar a ranar Laraba a yankin da ke kusa da iyaka da kasar Mali da masu ikirari na jihadi ke dabdalarsu.

https://p.dw.com/p/2vvWC
Mali Straße zur Grenze des Niger
Titin da ya hada iyakar Nijar da MaliHoto: picture-alliance/AP Photo/J. Delay

Jami'i da ke aiki da wata kungiya ta agaji an kama shi a kusa da Ayorou a yankin Tillaberi yankin da ke kara fiskantar hare-hare kan jami'an tsaro da sansanoni na 'yan gudun hijira. Kuma jami'in dan asalin Jamus ya gamu da wannan matsala ce lokacin da yake dawowa daga Ayorou kamar yadda Jando Rhichi Algaher ya fada wa kamfanin dillancin labaran AFP ta wayar tarho.

Ma'aikacin dai da abokan aikinsa sun fada wa mahukunta cewa za su yi tafiyar da safiyar ta Laraba acewar direbansu, sai dai lokacin da suke dawowa 'yan bindigar a babura hudu sun tsaresu inda suka yi gaba da jami'in daga Jamus bayan lallasa masu duka suka kuma kona motar.