1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Cika shekaru 30 da MDD ta yi ikirarin 'yancin yara

Abdourahamane Hassane
November 21, 2019

An cika shekaru 30 da Majalisar Dinkin Duniya ta cimma yarjejeniya game da hakkoƙin yara.Sai dai hakan na zuwa daidai lokacin da ake samun bayanai da ke nuna cewar ana azabtar da yaran a wasu sassan duniya.

https://p.dw.com/p/3TSlh
Karikatur: Nigeria Kinderrechte
Hoto: DW/Baba

Shekaru 30 bayan yarjejeniyar Majalisar Dinkin Duniya game da Hakkin yara, kasashe takwas na Afirka ne kawai suka dakatar da azabtar da yara, inda Afirka ta Kudu ta kasance karshe ta baya-bayan nan da ta shiga sahu a watan Satumba. Sai dai Burundi da Burkina Faso suna ci gaba da ba da izinin hukunta yara a gida ta hanyar. Yayin da Togo ta kasance ta farko a Afirka a 2007 da ta hana dukan yara kwata-kwata a gida ko a makaranta.