1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Tirka tirka a tattara sakamakon zaben Bayelsa

Muhammad Bello
November 13, 2023

Ana dab da kammala tattara sakamakon zaben gwamnan jihar Bayelsa bayan tsaikon isowar jami'an zabe daga kananan hukumomi da ke ruwa da kuma zargin tsakanin PDP da APC

https://p.dw.com/p/4YkOa
Mahmood Yakubu Shugaban hukumar zabe na Najeriya INEC
Mahmood Yakubu Shugaban hukumar zabe na Najeriya INEC Hoto: Kola Sulaimon/AFP/Getty Images

Tun a ranar lahadi ne dai jami'an zabe suka fara aikin karbar bayanan kuriun da a ka kada daga kananan hukumomi takwas da ke jihar ta Bayelsa. An dai ta samun tsaikon wannan aiki, a dalilai da wahalar isowar jamian zabe daga sassan kananan hukumomin bakin ruwa wato Riverine Communities,da kuma takaddama kan sakamakon zaben wasu kananan hukumomi biyu da ake zargi an yi aringizon kuriu da ya dara adadin ma su rajistar zabe, gami ma da zanga zanga da a ka yi ta yi a daura da hedikwatar hukumar zabe ta Jahar, kan zargin almundahana.

Zaben Najeriya 2023
Hoto: Benson Ibeabuchi/AFP

Mr Wilfred Ifoga, wani jamiin hukumar zabe da ke Bayelsa ya yi karin haske.

"Ya ce tuni aka kammala aikin kananan  hukumomi shida, kuma a ragowar biyun da ake dako, daya na gab da kammaluwa.

Kafin fara aikin tattara alkaluman zaben ragowar kananan hukumomin biyu dai, wato Brass da Ijaw ta kudu,a hukumance, PDP na da kuriu 137,909 APC na da 73,503.

Nigeria Benin City | Edo State Wahlen | Godwin Obaseki gewinnt
Hoto: Olukayode Jaiyeola/picture-alliance/dpa

A na dai sa ran kammala tattara alkaluman zaben na Bayelsa a wannan ranar ta Litinin tare da sanar da wanda ya lashe zaben kujerar gwamnan.

A can kuwa jihar Imo da tuni hukumar INEC ta sanar da Hope Uzodinma na jamiyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaben, bukukuwa kawai magoya baya ke yi, yayin da jamiyyun Labor da PDP ke ci gaba da watsi da sakamakon. Wasu 'yan jihar ta Imo da suke tsokaci sun baiyana bukatar sojoji da 'yan sanda su daina katsalandan a harkokin zabe, wanda suka ce ta haka ne za a gane masu hana ruwa gudu.