A cikin shirin za a ji cewa wasu da ake kyautata zaton ‘yan rajin kafa kasar Biafra ne sun kai wani hari a Hedikwatar rundunar 'yan sandan Najeriya da ke Jahar Imo, a yayin da a Jamhuriyar Nijar, batun fyaden da ake zargin wasu sojojin Chadi da yi wa wasu mata ne a yankin Tillabery ke ci gaba da daukar hankali.