Cikin shirin za a ji halin da mata 'yan hamayya suka shiga a Nijar bayan kame su da hukumomi suka yi. A Najeriya alkaluman marasa abin yi ne suka sake tashi inda miliyoyin 'yan kasar ke zaman kashe wando. Majalisar Dinkin Duniya ta shirya taron kawo fahimta tsakanin mabiya addinai da al'adu na duniya.