1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kasashen Turai sun nemi daukar mataki kan 'yan gudun hijira

Ramatu Garba Baba
September 5, 2018

Kasashen Turai sun soki Majalisar Dinkin Duniya kan gazawarta wajen isar da kayayyakin agaji ga dubban mabukatan da rikicin Boko Haram ya daidaita a Arewa Maso Gabashin Najeriya.

https://p.dw.com/p/34JQv
Flüchtlingscamp Menawo
Hoto: DW/M. Kindzeka

Mutum fiye da dubu dari takwas ne ke cikin tsananin bukatar abinci bayan da aka yanke hanyar isar da tallafin da ake basu,  kamar yadda ya ke kunshe a wasikar da kasashen suka aikawa majalisar.

Kasashen da suka kunshi Britaniya da Faransa da kuma Jamus dama kungiyar tarrayar Turai, sun nuna damuwa inda suka nemi majalisar da ta matsa kaimi don ganin gwamnatin Najeriya ta bayar da izinin isar da agaji ga 'yan gudun hijirar da ke a yankin da ya sha fama da rikicin mayakan kungiyar Boko Haram.

Wannan dai na a sabanin ikirarin da gwamnatin Najeriya ke yi, na cewa lamura sun koma yadda suke kuma jama'a sun fita daga cikin kangin da suka tsinci kansu a sanadiyar tashe-tashen hankula da suka biyo bayan ayyukan kungiyar masu tayar da kayar baya.