1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Legas: An fara sauraron korafin kisan 'yan #EndSARS

October 27, 2020

Kwamitin da gwamnatin jihar Lagos ta kafa domin sauraron korafe-korafe kan kisan gillar da ake zargin an yi wa wasu matasa, yayin zanga-zangar ENDSARS da ta rikide zuwa tarzoma ya fara zamansa.

https://p.dw.com/p/3kVRQ
Nigeria Lagos | Proteste gegen Polizeigewalt
Matasa na nun a goyon bayansu kan zanga-zangar kawo karshen SARS a NajeriyaHoto: Benson Ibeabuchi/AFP

Kwamitin karkashin jagoranci mai shari'a Doris Okuwobi ya zuwa yanzu ya karbi korafe-korafe har guda 15, kuma kwamitin zai kwashe tsawon watanni shida yana karbar korafin daga wadanda suka yi zargin aikata kisa a kan matasan da ke yin wannan zanga-zangar ta #ENDSARS, wadda ta rikide zuwa tashin hankali a jihar ta Lagos musamman a yankin Lekki, kuma zai rinka zaman sauraron korafe-korafen sau uku a kowacce rana.

Karin Bayani: Gwamnoni na musanta zargin boye kayayyakin tallafin abinci

Gwamnatin jihar ta Lagos ce dai ta kafa wannan kwamiti, bayan jerin korafe-korafe da aka yi mata dangane da zargin jami'an tsaro da aikata kisan gilla a kan matsan da ke zanga-zangar ganin an rushe rundunar 'yan sandan musamman masu yaki da fashi da makami a kasar, wato SARS.

Nigeria l Nach Protesten in Lagos, Verletzte im Krankenhaus
Gwaman Lagos Babajide Sanwo-Olu ya ziyarci wadanda suka jikkata a zanga-zangarHoto: Ademola Olaniran/Lagos State Government/Reuters

Zanga-zangar dai mai taken #ENDSARS, da aka rinka gudanar da ita a Najeriya baki daya, ta rikide ya zuwa tashin hankali a wasu sassan kasar ciki kuwa har da jihar ta Lagos. 

Karin Bayani: Ana cigaba da mayar da martani kan jawabin Buhari

Mai shari'a Okuwobi dai, ta bukaci duk wanda yake da korafi dangane da kisan da aka yi wa masu zanga-zangar ta neman kawo karshen rundunyar 'yan sandan ta SARS, ya garzaya ya zuwa gareta domin gatar da shi. Sai dai masu fashin baki kan al'amuran yau da kullum na ganin kwamitin duk da bayyana kudirinsa na tabbatar da adalci da ya yi, yana da jan aiki a gabansa ganin cewa baya ga kisan ba gairan da ake zargin jami'an tsaro da aikatawa, su ma fa masu zanga-zangar sun yi ta wasoson kayan jama'ar da ba su ji ba su gani ba.