Yadda wasanni suka kaya a karshen mako
March 23, 2026
An kammala wasannin na karshen mako a Jamus kamar haka:
Wolfsburg 0 Werder Bremen 1
Heidenheim 3 Bayer Leverkusen 3
Cologne 3 Moenchengladbach 3
Borussia Dortmund 3 Hamburg 2
St Pauli 1 Freiburg 2
Augsburg 2 Stuttgart 5
Mainz 2 Frankfurt 1
Kungiyar Enugu Rangers tana kara karfafa matsyinta a samun teburin na Najeriya, yayin da Ahmed Musa kuma yake ci gaba da nuna bajinta cikin kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars. Ga dai yadda sakamakon wasannin NPFL na Najeriyar a mako na 31 ya kasance:
Wikki Tourist FC 0-0 Barau FC
Katsina United FC 1-0 Shooting Stars SC
Plateau United FC 1-0 Bayelsa United FC
Rangers FC 2-0 El-Kanemi Warriors FC
Kano Pillars FC 2-0 Enyimba FC
Kun Khalifat FC 2-2 Ikorodu City FC
Warri Wolves FC 0-0 Bendel Insurance FC
Remo Stars SC 3-1 Kwara United FC
Jagoran 'yan wasan Maroko, Achraf Hakimi ya yi watsi da nasarar da kotu ta bai wa kasar na lashe kofin Afirka, maimakon Senegal da ta dauki kofin. Kuma ya dage cewa Senegal ce ta yi nasara a filin kwallo maimakon bai wa kasarsa kofin sakamakon nasara a kotu. Hakimi ya kara da cewa mahaifiyarsa ta shaida masa cewa kar ya amince da nasarar da hukumar kwallon kafa ta Afirka ta bai wa Maroko kofin maimakon Senegal da ta yi nasara a fagen kwallon, kuma kan haka ya tsaya. Sannan ya ce Senegal ta samu nasarar da ta dace kan kasarsa ta Maroko.
An kammala gasar cin kofin kwallon kafa na matan Asiya a birnin Sydney inda a wannan karon ma kasar Japan ce ta dauki kofin bayan da ta tashi da ci ba ko daya tsakaninta da Ostiraliya a wasan karshe. Wannan ne karo na uku da take daukar kofin bayan da ta yi nasara a shekarar 2014 da 2018.