1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

2023: Wakilan jam'iyyu sun yi dandazo a Abuja

Uwais Abubakar Idris ZUD
May 19, 2022

Babban birnin Najeriya, Abuja, ya tumbatsa da masu zaben fitar da gwani da a cikin 'yan kwanaki masu zuwa za su zabi dan takarar da manyan jam'iyyun APC da PDP za su tsayar takarar shugaban kasa a zaben 2023.

https://p.dw.com/p/4BbA4
Nigeria Benin City | Edo State Wahlen | Godwin Obaseki gewinnt
Hoto: Olukayode Jaiyeola/picture-alliance/dpa

Wadannan 'yan siyasa da ke zama wakilan da za su zabi wadanda za su yi wa jam'iyyunsu takara sune a yanzu tutarsu ke kadawa a fagen siyasar Najeriyar, domin suke rike da sandar duka ta zaba wa kasar makoma. 

A baya dai yunkuri na kawar da amfani da wakilai a zaben fitar da gwani ya kasa samun nasara, abin da ya sanya su zama wadanda a yanzu ake masu kallon masu rike da akalar siyasar kasar kafin aje babban zaben shekara mai zuwa. Yawaitarsu a birnin Abuja, ta sanya tuni  manyan otel-otel suka zama matattara ta 'yan siyasa, inda 'yan takara ke bin su suna kamun kafa. Ana kuma zargin amfani da kudade a kokarin samun goyon bayan 'delegate' din a dukkanin manyan jam'iyyun kasar.

A bana ne dai Shugaba Muhammadu Buhari na Najeriya ya rattabu hannu kan dokar zabe, wacce ake sa ran za ta samar da gyare-gyare a wurin zaben fitar da gwani. To ko hakan za ta samar da sauyin da ake bukata a yanzu da ake 'yan kwanaki kafin a fara zaben fitar da gwanin? 

Hukumar zaben Najeriya, INEC, ta bukaci jam'iyyun kasar su kammala zabukan fitar da gwanin nan da makon farko na watan Yuni mai kamawa. 

Tsallake zuwa bangare na gaba Bincika karin bayani

Bincika karin bayani