1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Nijar ta kamalla shirin gudanar da zaben zagaye na biyu

Ramatu Garba Baba
February 18, 2021

A yayin da ake shirin gudanar da zabe a zagaye na biyu, a jihar Maradi, dan takara Mahamane Ousmane ya sami karin magoya baya.

https://p.dw.com/p/3pYtm
Bildkombo Niger | Mohamed Bazoum und Mahamane Ousmane

Magoyan jam’iyyar MNSD Nasara reshen jihar Maradi sun fidda sanarwar ta goyan bayansu ga dan takara Mahamane Ousmane a zagaye na biyu na zaben shugaban kasa da ke tafe.

Abun jira a gani dai, shi ne tasirin ko akasin haka da wannan goyan bayan zai yi a ranar 21 Febrairu mai zuwa, da ake gudanar da babban zaben zagaye na biyu.