1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Venezuela ta sallami jakadan Jamus

March 6, 2019

Gwamnatin Venezuela ta sanar da korar jakadan Jamus da ke a kasarta saboda zargin tsoma baki da ya yi cikin harkokin kasar.

https://p.dw.com/p/3EZ1d
Daniel Kriener, jakadan Jamus a Venezuela
Daniel Kriener, jakadan Jamus a VenezuelaHoto: Imago/V. Sharifulin

Gwamnatin Shugaba Nicolas Maduro, ta debar wa jakadan na Jamus Daniel Kriener sa'o'i 48 da ya bar kasar, saboda saba ka'idojin tsarin diflomasiyyar kasashe.

Sallamar jakadan na Jamus a Venezuela dai na zuwa ne kwanaki biyu da marabtar madugun adawar kasar Juan Guaido da ya yi, a filin jirgi na birnin Caracas.

Tuni kuwa ma'aikatar harkokin wajen Jamus ta sanar da labarin sallamar babban jami'in na ta na diflomasiyya a Venezuelar, tana mai cewa tana kan tuntubar kawayenta dangane da wannan batu.

Kasar Venezuela dai na cikin rikicin shugabanci, inda wasu manyan kasashen duniya suke goyon kawo karshen mulkin Shugaba Nicolas Maduro tare da amince wa Juan Guido ya rike gwamnatin riko.