Jamus da Turkiyya na taro kan makamashi
October 26, 2018Talla
A jawabinsa yayin bude taron, Altmaier ya yi karin haske dangane da kokarin bunkasa dangantakar sabunta makamashin da ke tsakanin kasashen biyu. Altmaier ya kara da cewa Turkiyya da Jamus za su zamo abin kwatance dangane da batun na sabunta makamashi, yana mai yabawa mahukuntan na Ankara bisa kudirinsu na kasancewa wata cibiya ta samar da makamashin iskar gas tsakanin Turai da Asiya. Baki dayan kasashen biyu dai na Jamus da Turkiyya na dogara ne da shigo da makamashin iskar gas din daga kasar Rasha.