A cikin shirin za a ji a cigaba da kokarin neman mafita kan rikicin makiyaya da manoma, gwamnonin jihohin arewacin Najeriya sun amince da kaddamar da shirin inganta harkokin kiwo da ke da zummar tsugunar da masu sana'ar kiwon a jihohin yankin. A jamhuriyar Nijar kuwa jami'iyyar CDS Rahama ta cimma yarjejeniyar dinke barakar da take fama da ita.