A cikin shirin za a ji cewa -Jaruman fina-finan Hausa a Najeriya sun bayyana damuwa kan matsalolin tsaro a yankin arewacin Najeriya da ke neman ya gagari kundila, a yayin da -A Jamhuriyar Nijar, manoma suka fara nuna fargaba dangane da yadda sauyin yanayi ya fara tasiri kan al’amarin noma musamman ma manoman da ke da gonaki a yankin da ake tace man fetur din kasar a yankin Damagaram.