A cikin shirin za a ji cewa Masu fashin baki da 'yan siyasa da ma sauran al'umma a Jamhuriyar Kamaru na ci gaba da tofa albarkacin bakunansu kan kisan da 'yan awaren kasar ke cigaba da yi wadanda suke zargi da bada bayanan sirri a kansu. Al’umma a yankin Diffa da ke fuskantar hare-haren 'yan bindiga sun fara cire fargaba da tsoro daga zukatansu.