1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sankarau na ci gaba da kisa a Najeriya da Nijar

May 12, 2017

Kungiyar likitoci masu bayar da agaji ta duniya ''Doctors Without Borders'' ta fitar da rahoton cewar cutar Sankarau da ta kashe akalla mutane 836 a Najeriya, ita ce mafi muni da aka samu tun farkon shekara ta 2016.

https://p.dw.com/p/2csl5
Elfenbeinküste Krankenhaus
Hoto: Getty Images/AFP/S. Kambou

A cewar rahoton kungiyar ta Medicine Sans Frontairs a turancin faransa, akalla mutane 10,000 ne suka kamu da cutar ta sankarau rukunin C wadda kuma ita ce mafi hatsari a Najeriya a wannan shekara kadai.

Rahoton ya ce jihohin Sokoto da Zamfara da ke yankin arewa maso yammacin Najeriya ne cutar ta fi kamari cikinsu a kwanakin baya, inda masu kamuwa da ita kan rasa karfin garkuwar jiki, da raunin kwakwalwa da kuma na laka.

Hukumomi a tarayyar ta Najeriya dai na bayyana nasarar kakkabe cutar baki daya, amma ga alama akwai sauran rina a kaba. A wata ziyara da DW ta kai kauyen Bagarawa na karamar hukumar Bodinga a jihar Sokoto, mutanen kauyen sun ce har yanzu cutar na nan cikin jama'a.

Ärzte ohne Grenzen Südsudan Flüchtlinge Februar 2014
Hoto: AFP/Getty Images/H. Mcneish

Rahoton na Medicine Sans Fronteirs, haka nan ya bayyana shakku a kan karancin magungunan sabuwar cutar da aka yiwa lakabi da type C a dai dai lokacin da cutar ke ci gaba da kashe mutane. Ko a kwanakin nan ma inji mazauna kauyen Bagarawa an rasa rayuka a sakamakon wannan cuta.

Sai dai a ta bakin kwamishinan lafiya na jihar Sokoto Dr. Balarabe Shehu Kakale, sankarau ta zama tarihi a jihar Sokoto idan aka yi la'akari da kwararan matakan da gwamnati ta dauka.

Cutar ta sankarau dai cuta ce mai saurin yaduwa da kisan jama'a cikin hanzari.