1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Bude sabon babin huldar tsakanin EU da AU

Gazali Abdou Tasawa
January 10, 2020

Ministan raya kasashe na kasar Jamus, Gerd Müller ya bayyana bukatar bude wani sabon babin huldar kasuwanci tsakanin Kungiyar Tarayyar Turai da kuma nahiyar Afirka.

https://p.dw.com/p/3VziS
Deutschland Bundesminister für wirtschaftliche Zusammenarbeit und Entwicklung Gerd Müller
Hoto: picture-alliance/dpa/K. Nietfeld

Shirin wanda zai hada a wuri daya batun yaki da yinwa da kuma talauciya, da huldar kasuwanci da batun 'yan gudun hijira da yaki da gurbatar muhalli, tanadi cimma yarjejeniya tsakanin kungiyar ta EU da kuma takwararta ta AU a karkashin jagorancin kasar Jamus.

 Tuni dai majalisar dokokin Turai ta sanya hannu kan kudirin dokar kafar sabuwar huldar wacce amma za ta bayar da muhimmanci ga batun mutunta hakkin dan Adam wajen aiwatar da ita.