1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jamus ta musanta sabuwar yarjejeniya da Girka

Yusuf BalaFebruary 10, 2015

Wolfgang Schaeuble ministan kudin Jamus ya ce babu gaskiya a rahotannin da ke fita cewa kasar Girka ta shiga sabuwar tattaunawa da kasashen da ke binta bashi.

https://p.dw.com/p/1EZGU
Berlin Steuerkonferenz 2014
Wolfgang Schaeuble: Ministan harkokin kudin JamusHoto: Tobias Schwarz/AFP/Getty Images

Ministan harkokin kudin Jamus Wolfgang Schaeuble a yau Talata ya bayyana cewa babu wani sabon shiri kan tallafa wa tattalin arzikin Girka inda ya ce ya zama wajibi a fara daddalewa akan shirin da aka fara karon farko.

Da yake jawabi a wajen taron ministocin harkokin kudade daga kungiyar kasashe masu karfin tattalin arziki na G20 da ke wakana a birnin Istanbul na kasar Turkiya ya bayyana cewa babu kanshin gaskiya a rahotannin da ke fita cewa kasar Girka ta shiga sabuwar tattaunawa da kasashen da ke binta bashi.

Ya ce babu wata sabuwar yarjejeniya da suka shiga, tuni suna da shirin da suke kansa a yanzu za kuma a sake tattaunawa a kansa a taron ministoci na kungiyar ta EU da za a yi anan gaba cikin wannan mako.