Jamus: Adawa da wasu matakan dakile corona | Labarai | DW | 16.05.2020
  1. Inhalt
  2. Navigation
  3. Weitere Inhalte
  4. Metanavigation
  5. Suche
  6. Choose from 30 Languages

Labarai

Jamus: Adawa da wasu matakan dakile corona

Ana sa ran duban jama'a za su fito yin zanga-zanga a wasu jihohi dabam-dabam na tarayyar Jamus don nuna rashin jin dadinsu kan matakan takaita zirga-zirga da hukumomi ke dauka don dakile Covid-19.

Rahotanni daga sassan kasar Jamus sun ce masu akidar tsananin kyamar baki da dama ne ake hasashen za su fito don yin zanga-zangar a karshen wannan mako ciki har da jihohin Munich da Dortmund da ma babban birnin kasar wato Berlin.

Akalla mutun dubu biyar ne suka fito yin boren a baya a birnin Stuttgart, duk da matakin hana yin duk wani taron da ke tara jama'a da hukumomin kasar suka yi a baya.

Masu boren dai na ci gaba ne da nuna kyama kan matakan gwamnatin kaar da suka kira na hana walwala da 'yan cin jama'a.