1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Girka: Jamus ta amince da tallafin ceto

Ahmed SalisuAugust 19, 2015

Majalisar dokokin tarayyar Jamus ta kada kuri'ar amincewa da tallafin ceto tattalin arziki kashi na uku da aka baiwa kasar Girka wadda tattalin arzikinta ke tanga-tangal.

https://p.dw.com/p/1GHrP
EU Gipfel zu Griechenland in Brüssel
Firaministan Girka Alexis Tsipras da shugabar gwamnatin Jamus Angela MerkelHoto: Reuters/Y. Herman

Shugaban Majalisar dokokin ta Bundestag Norbert Lammert ya ce daga cikin 'yan majalisa 585, mutum 454 sun amince da wannan kuduri, 113 sun kada kuri'ar rashin amincewa yayin da mutum 18 suka yi rowar kuri'unsu.

Ministan kudin Jamus kana mamba na majalisar ta Bundestag Wolfgang Schaeuble ya ce da tallafin takwarorinta na kungiyar kasashen Turai da ke amfani da takardar kudin euro, Girka ta sake samun damar da za ta iya amfani da ita wajen ceto tattalin arzikinta.