1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Gidauniyar Jamus ta karrama matan Kamaru

June 6, 2023

An karrama wasu mata 32 a Kamaru da lambar yabo da gidauniyar Jamus ke bai wa wadanda ke kokari ta fannin tabbatar da zaman lafiya a nahiyar Afirka.

https://p.dw.com/p/4SH0a
Jamus ta karrama mata 'yan gwagwarmaya a Kamaru
Hoto: Elisabeth Asen/DW

Matan da suka samu wannan nasara, na daga cikin matan da ke fadi tashin ganin an zauna lafiya a Kamarun.

Gidauniyar Jamus da takarrama matan su 32, ta kwashe shekaru 45 tana wannan aiki da zimmar kyautata dangantaka tsakanin Jamus da kasashen nahiyar Afirka.

Yankunan kasar Kamaru 10 dai na fama da matsalolin tsaro, inda galibi mata ne suka fi fama da wahalhalun da rashin kwanciyar hankalin ke haifarwa.

Dukkanin matan da suka yi wannan nasarar dai sun nuna farin cikinsu, musamman ganin irin gwagwarmayar da suke sha a kungiyance wajen ganin an samu zaman lafiya a kasar.