1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Yan Najeriya 30,000 sun yi kaura zuwa Nijar

June 16, 2020

Majalisar Dinkin Duniya ta ce akalla mutane 30,000 ne suka kaurace wa gidajensu a Najeriya suka koma Jamhuriyar Nijar domin neman mafaka.

https://p.dw.com/p/3dsdo
Niger Bevölkerungswachstum Frau mit Kindern
Hoto: Getty Images/AFP/O. Omirin

Syldie Bizimana jami'in majalisar a jamhuriyar Nijar ya ce wannan kaura ta wakana ne a cikin watanni biyu da kauyukan mutanen ke fuskantar hare-haren 'yan bindiga.

''Mutanen sun samu mafaka a kauyukan Nijar na bakin kan iyaka duk da muna kula da wasu daga cikinsu ba zamu iya karesu ba. Akwai mata da kananan yara a cikin wadannan mutane. Gaskiya sun shiga mawuyacin hali.'' inji Mista Bizimana.

Majalisar Dinkin Duniya ta ce mutanen da suka yi kaura zuwa Nijar a baya-bayan nan sun fito ne daga jihohin Katsina da Zamfara da kuma Sokoto. Majalisar ta ce kashe-kashe da garkuwa da mutane gami da hare-hare babu kakkautawa suka tilastawa mutanen barin gidajensu don tsira da rayuwarsu.