1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Dubban mutane na tserewa daga Afrin

Zainab Mohammed Abubakar
March 21, 2018

Gwamnatin Jamus ta bayyan damuwa kan karin hare-hare da sojojin Turkiyya ke kaiwa a birnin Afrin da ke yankin Arewacin Siriya, tare da kira ga Turkiyyar da ta darajawa dokokin kasa da kasa da ke kare fararen hula.

https://p.dw.com/p/2uhzK
Syrien Familie in Afrin
Hoto: Reuters/K. Ashawi

Mai magana da yawun  gwamnati Ulrike Demmer ta ce, su na bin diddigin rahotannin yadda Turkiyyar ta kwace mafi yawan garuruwan da ke yankin, kuma abun takaici ne yadda dubban mutane ke tserewa domin neman mafaka saboda halin da ake ciki a birnin na Afrin.

Tuni dai ma'aikatar harkokin wajen na Jamus ta yi kira da a gudanar da binciken rahotannin irin kisan kiyashi da dibar ganima da ke gudana a Afrin, tare da hawa teburin sasanta wannan rikici da Siriya.

Dubban 'yan gudun hijira ne dai ke cigaba da ficewa daga garin wadanda akasarinsu mata da kananan yara ne, saboda kazamin fada da ake gwabzawa.