1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Buhari ya sha rantsuwar wa'adin mulki na biyu

Abdul-raheem Hassan
May 29, 2019

'Yan Najeriya dai na fatan shugaban ya sauya salon yaki da matsalar tsaro ta satar mutane da rikicin manoma da habaka tattalin arzikin kasar da samar da ayyukan yi.

https://p.dw.com/p/3JRzS
Präsident von Nigeria Muhammadu Buhari
Hoto: picture-alliance/AP Photo/S. Alamba

A ranar 29 ga watan Mayu na shekarar 2019 Shugaba Mohammdu Buhari ya sha rantsuwar fara wa'adin mulki na biyu na wasu shekaru hudu. Jam'iyyar APC mai mulki a Najeriyar na cike da fatan mataki na gaba na  samar wa kasar mafita kan tarin matsaloli da ake fama. Shugaba Buhari mai shekari 76 na ikirarin karya lagon mayakan Boko Haram a wadin mulkinsa na farko, sai dai 'yan adawa na kalubalantar nasarar shugaban a wannan bangare.