An gaza samun mafita kan nadin jiga-jigan EU
July 1, 2019Talla
Shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel ta bayyana fatan cimma matsaya game da nada jigajigan kungiyar Tarayyar Turai. Wannan ya biyo bayan dage taron shugabanni kasashen Tarayyar Turan da ake gudanarwa a birnin Brussels na kasar Belgiyam izuwa Talata mai zuwa.
Tattaunawar ta yi tsauri a cewar Angela Merkel amma tana kyautata zaton za a cimma matsaya idan duk bangarorin suka nuna sanin ya kamata.