1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jamus ta gargadi 'yan gudun hijirar Siriya

Ramatu Garba Baba
August 18, 2019

Ministan harkokin cikin gidan Jamus Horst Seehofer, ya ce za a iya janye takardar shedar zaman dan kasa na duk dan asalin Siriya da aka gano na yawan kai ziyara kasar.

https://p.dw.com/p/3O52w
Horst Seehofer
Hoto: picture-alliance/dpa/K. Nietfeld

Horst Seehofer, ya fadi hakan ne a yayin tattaunawa da jaridar kasar mai suna Bild am Sonntag, ya ce shawarci daukar matakin ne kan duk wani dan asalin kasar Siriya, da aka gano na yawan kai ziyara kasar  bayan da ya nemi mafaka daga rikici.  Ministan ya ce, muddun dan gudun hijira na iya kai da kawo wa a kasar, to ashe babu sauran barazanar da ya ke fuskanta, saboda haka dole Jamus ta dauki matakin janye takardar shedar zaman da ta bayar.

Yanzu haka ana sa ido kan rikicin na Siriya kuma da zarar an gamsu da wanzuwar tsaron kasar, za a soma mayar da 'yan gudun hijirar, inji ministan. 'Yan Siriya fiye da dubu dari bakwai ne suka tsere daga kasar zuwa Jamus, a tsawon shekaru takwas da yakin basasa ya barke.