1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An bukaci Jamus ta tsananta kare baki

Zulaiha Abubakar
February 21, 2020

Kurdawa mazauna Jamus sun bukaci gwamnati ta dauki matakai kan masu akidar kyamar baki yayin da suke alhinin mutuwar mutane tara da dan bindiga ya harbe a wasu shagunan shan shiha a garin Hanau da ke tsakiyar kasar.

https://p.dw.com/p/3Y72Q
Hanau Gedenken deutschlandweit  / Berlin
Hoto: Reuters/C. Mang

Tun a jiya Alhamis da balahirar ta afku Shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel tare da Shugaban kasar Frank-Walter Steinmeier suka yi Allah wadai da muggan dabi'un, tare da jaddada aniyar hukuma na yaki da tashin hankali a fadin kasar a lokacin da suke zagayen jajantawa al'umma. To amma wani mai magana da yawun Kurdawan Ayten Kaplan mazaunin Gabashin Jamus ya bayyana cewar jaddada akidar kawo karshen irin wadannan hare-hare ba za su yi maganin komai ba, don haka ya zama wajibi shugabanni a Jamus su kare rayukan Musulmi da Yahudawa daga masu kyamar baki da suke kai hari.