Zaben majalisa a Masar
June 11, 2007Talla
Jamiyar masu kishin islama ta Muslim Brotherhood a kasar Masar tace yan sanda sun lallasa tare da tsare wakilanta a yayinda ake zaben majalisar dokoki ta kasar a yau.
Rahotanni daga birn9in alkahira sunce yan sandan sun hana wasu yan jamiyar ta yan uwa musulmi fita jefa kuriarsa.
Mutum guda dai ya rasa ransa cikin musayar wuta tsakanuin magoya bayan jamiyar dake mulki ta NDP da na wani dan takara mai zaman kansa a lardin Sharkia .
An shirya zaben na yau ne karkashin wani gyara da akayiwa kundin tsarin mulkin kasar