Za a kara agaji a Ghouta
March 8, 2018Talla
Hare-haren na kasashen biyu sun janyo martani daga kasashen duniya, baya ga amincewar da Majalisar Dinkin Duniya na a tsagaita budawa juna wuta, abin ma da ya kai MDD ga bayyana hakan a matsayin mataki ne na neman ruguza gabashin na Ghouta baki daya.
Alkaluma dai sun yi nunin cewa sama da mutum 860 ne suka mutu, wasu da dama kuwa na fama da raunuka tun bayan kaddamar da wuta da gwamnati shugaba Assad ta yi a ranar 18 ga watan jiya. Gabashin na Ghouta da ke wajen birnin Damascus, waje ne da gwamnatin ta Syria ke cewa da ya saura a hannun mayakan tawaye.