1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Karuwar hare-haren Boko Haram a Najeriya

November 22, 2018

Ministan tsaron Najeriya yana kan hanyar zuwa kasashen Chadi da Kamaru da nufin tattaunawa bayan wani sabon hari ya hallaka sojojin Najeriya da daman gaske cikin wannan makon a Arewa maso Gabashin Najeriya

https://p.dw.com/p/38kJW
Mutmaßlicher Boko-Haram-Angriff in Nigeria
Hoto: picture-alliance/AP/Jossy Ola

Dangane da yadda ake samun yawaitar kai hare-haren ta'addanci daga kungiyar Boko Haram a yankin arewa maso gabashin Najeriya, ministan tsaron Najeriya ya doshi kasashen Chadi da Kamaru da nufin tattaunawa kan batun biyo bayan hallaka sojojin Najeriya masu yawan gaske a cikin wannan makon da ake zaton yawansu ya kai kimanin 44, a harin da kungiyar ta kai a wasu kauyuka masu iyaka da jamhuriyar Nijar.

'Ya'yan kungiyar ta ta'adda dai sun share kwanaki dai dai har guda uku, suna hari a sansanin sojojin tarrayar Najeriyar guda uku a kauyen Matele a farkon mako. Yanayin da ya janyo tada hankali har a Abuja inda ministan tsaron na tarayyar Najeriya janar Mansur Dan Ali ya yi wata ganawar sirri da shugaban kasar a kan batun.

Mutmaßlicher Boko-Haram-Angriff in Nigeria
Hoto: picture-alliance/AP/Jossy Ola

Janar dan Alin dai ya ta'allaka sabbabin hare-haren a kan sojin kasar da janyewar sojojin Chadi da ke bada kariya ga sojin tarrayar Najeriyar daga baya. ko bayan matsalar janyewar Chadin, ana kuma kallon share tsawon lokaci wuri guda a bangare na sojin tarrayar Najeriyar na haifar da karin gajiya a bangare na sojojin da wasunsu sun share shekaru suna filin dagar mai hatsari. A dai bayaninsa, ministan ya ce suna kokarin tunkarar  matsalar da gaggawa.

A baya dai manyan hafsoshin sojin kasar, sun dauki lokaci suna ikirarin cin dunduniyar kungiyar, kafin sababbabin hare-haren da ke nuna jan aikin da ke gaban mai gona, a kokari na kai biri gidan tarihi.Ko da yake ministan ya ce sabbabin hare-haren ba alama bace ta fin karfin sojin, daga bangaren Boko Haramun din da ke dada nuna karfinsu.

Sabbabin hare-haren da ke zuwa a dai dai kadowar siyasar kasar dai, na zamewa sabuwar barazana ga tarrayar Najeriyar da ke fatan zabe a ko'ina a cikin hali na lafiya, amma kuma ke kallon wannan annoba ce da ke neman kunno kai.