1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Turai za ta taimaka wa Kurdawan Iraki

August 11, 2014

Faransa ta bukaci kasashen EU su tallafa wa Kurdawan Iraki

https://p.dw.com/p/1CsTv
Irak Jesiden Flucht 10.8.2014
Hoto: Reuters

Ministan harkokin wajen Faransa Laurent Fabius ya fadi a wannan Litinin cewa kamata ya yi kasashen kungiyar Tarayyar Turai na EU, su amsa kiran Kurdawa 'yan Iraki na a tallafa wa mayakan su da kayan yaki dan tunkarar mayakan IS.

A cikin wata wasika da ya aike wa babbar jami'ar kula da harkokin wajen keatere ta kungiyar EU, Catherine Ashton, Fabius ya ce abu ne mai mahimmanci daga yanzu kasashen na Turai su tashi dan ba da wannan tallafi.

Mawallafi: Yusuf Bala
Edita: Suleiman Babayo