1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaTurai

Turai za ta kai Turkiyya kotu kan hakkin dan Adam

December 3, 2021

Majalisar Turai ta Council of Europe da ke fafutukar kare hakkin dan Adam a nahiyar Turai ta ce za ta kai Turkiyya kotu kan ci gaba da rike attajirin nan na Turkiyya Osman Kavala tsawon shekaru hudu.

https://p.dw.com/p/43nN6
Belgien | Pressekonferenz Ursula von der Leyen und Charles Michel nach Treffen mit Erdogan
Hoto: Reuters/F. Lenoir

Majalisar ta Turai ta zargi Turkiyya da watsi da hukuncin kotun Turai na 2019 da ya bukaci Turkiyyar ta saki Kavala tun da ba a kama sa da wani laifi a hukumance ba. Sai dai gwamnatin Turkiyya ta gargadi majalisar Turan da cewa wannan yunkuri ne na yi mata shisshigi kan harkokinta na cikin gida.


Tun a shekara ta 2017 ne dai gwamnatin Turkiyya ta kama Osman Kavala bisa zargin sa da hannu a wata zanga-zangar kin jinin gwamnati da aka yi a shekara ta 2013. Kazalika gwamnatin Shugaba Erdogan na zargin Kavala da bayar da gudunmawa wurin juyin mulkin da bai yi nasara ba a shekara ta 2016.