1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sojoji sun gano gawawwaki a Damasak

Muntaqa AhiwaMarch 21, 2015

Sojojin Nijar da na Chadi sun gano wasu gawawwaki masu yawa a garin Damasak na jihar Borno da ke Tarayyar Najeriya bayan sun kwato garin a hannun 'yan Boko Haram

https://p.dw.com/p/1EutH
Tschad Fahne Soldaten Kampf gegen Boko Haram Nigeria
Hoto: Reuters/Emmanuel Braun

Dakarun kasashen Nijar da Chadi da suka kwato garin Damasak na jihar Bornon Najeriya daga hannun mayakan Boko Haram, sun ce sun ga wasu gawawwakin mutane masu yawa a yashe karkashin wata gadar dake yankin na Damasak, da suka yi imanin cewa mayakan Boko Haram ne suka halaka su.

Kamar dai yadda wani sojan Chadi ya shaidar, ya ce sun ga akalla gawarwakin mutane 100 a gadar, da wani daga cikinsu da aka yiwa yankan Rago.

Sai dai alamun da ke wajen na nunin cewa, wannan danyen aikin ya dan kwana biyu saboda irin bushewar da gwawarwakin suka yi.

Daga cikin gawawwakin harma da ta wani limamin garin.