1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Bincike kan satar bayanai a Jamus

Zulaiha Abubakar
January 7, 2019

Ministan cikin gida na Jamus Horst Seehofer ya sha alwashin yin gamsasshen bayani game da satar bayanan 'yan siyasar kasar da ya afku a makon daya gabata.

https://p.dw.com/p/3B7on
Horst Seehofer Bundesinnenminister
Hoto: Getty Images/S. Gallup

Ministan zai gana da shugabannin ofishin lura da aikata manyan laifuka da na tsaron kafafen sadarwar Internet domin jin sakamakon binciken da suka gudanar da kuma hanyoyin magance matsalar, inda ya yi alkawarin sanarwa da al'ummar kasar batutuwan da suka tattauna yayin taron.

Wannan dai shi ne kutse mafi muni da ya taba faruwa a kasar. Masu kutsen dai sun saci bayanan 'yan siyasar kasar kuma suka watsa a shafin Twitter. Wadanda wannan lamari ya shafa sun hada da shugabar gwamnatin Jamus dain Angela Merkel da shugaban kasa Frank-Walter Steinmeier da 'yan majalisu da 'yan jaridu da kuma wasu fitattun mutane.