1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

MDD ta ce a bincika kashe-kashen jama'a a Najeriya da Chadi

May 14, 2026

Majalisar Dinkin Duniya ta bukaci a gudanar da bincike kan mutuwar fararen hula a hare-haren sama da sojojin Najeriya suka kai a Zamfara, inda rahotanni suka ce fiye da mutane 100 ne suka mutu.

https://p.dw.com/p/5DlPJ
Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya, António Guterres
Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya, António GuterresHoto: Fabrice Coffrini/AFP/Getty Images

Majalisar Dinkin Duniya ta bukaci da a gudanar da bincike kan bayan hare-hare ta sama da sojojin Najeriya da Chadi suka kai wanda ya shafi fararen hula.

Kungiyar kare hakkin bil Adama ta Amnesty International da mazauna sun ce harin saman da sojojin Najeriya suka kai wata kasuwa a jihar Zamfara ya kashe akalla mutane 100, galibinsu fararen hula ne.

Babban kwamishinan kare hakkin bil Adama na Majalisar Dinkin Duniya Volker Türk ya bayyana damuwa kan girman asarar rayuka tare da kira ga kasashen biyu da su tabbatar da daukar alhakin lamarin.

Rahotanni sun kuma ce hare-haren saman Chadi a yankin Tafkin Chadi kan sansanonin Boko Haram sun kashe wasu masunta ‘yan Najeriya da dama.

Majalisar Dinkin Duniya ta jaddada cewa wajibi ne sojoji su kare fararen hula tare da bin dokokin kasa da kasa yayin gudanar da hare-hare.