'Yan bindiga sun kashe sojojin Mali 24
November 19, 2019Talla
Rundunar tsaron Mali ta ce harin ya jikkata wasu 29 an kuma kashe maharan da dama tare da kama daruruwansu, harin ya zo ne bayan wasu hare-hare da ya kashe sojojin kasar da dama a farkon wata.
Tun shekarar 2012 arewacin Mali ke fama da barazanar rashin tsaro duk da fafutukar dakarun hadin gwiwa da Faransa ke jagoranta, amma haryanzu kan iyakar Mali da Nijar da Burkina Faso na fama da barazanar 'yan ta'adda.