1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jamus ta rufe mahakar ma'adanin kwal ta karshe

Abdullahi Tanko Bala
December 22, 2018

Gwamnatin Jamus ta rufe mahakar ma'adanin kwal ta karshe da aka shafe kimanin shekaru 200 ana hakar kwal a ciki a birnin Battrop dake jihar North Rhine Westphalia

https://p.dw.com/p/3AUds
Deutschland Zeche Prosper-Haniel | Übergabe letztes Stück Steinkohle an Bundespräsident Steinmeier
Hoto: Reuters/T. Schmuelgen

Shugaban kasar Jamus Frank Walter Steinmeier ya jagoranci bikin rufe mahakar ma'adanin a yankin masana'antu na Rhur mai dadadden tarihi.

Gwamnatin tarayya da Jihohin North Rhine Westphalia da Saarland tare da kungiyoyin hakar ma'adanai ta IG BCE sun cimma yarjejeniya a shekarar 2007 domin kawo karshen hakar ma'adanin na kwal.

Fannin hakar kwal din dai ya samar da guraben ayyuka ga mahaka ma'adanai kimanin 33,000

Shugaban hukumar tarayyar Turai Jean Claude Juncker da Firimiyan jihar North Rhine Wesphalia na daga cikin wadanda suka halarci bikin.

A shekarar 1951 ne dai kasashe shida na tarayyar Turai da suka hada da Jamus da Italiya da Faransa Belgium da Netherlands da kuma Luxemburg suka sanya bangaren hakar ma'adanin kwal din karkashin hukuma guda ta ma'adanin kwal da karafa.