Jamus ta fiskanci kutsen na'urorin kwamfuta
February 28, 2018Talla
Mai magana da yawun ma'aikatar harkokin cikin gidan Jamus ya ce ma'aikatun gwamnati da aka yi wa kutsen cikin na'urorinsu na kwamfuta sun binciki lamuran sun kuma kare bayanansu.
Ya dai kauce wa yin tsokaci na kafafan yada labarai na Jamus cewa kutsen Rasha ke da hannu a ciki, wacce ko a shekarar 2015 ta yi kutse irin wannan a majalisar dokokin kasar ta Jamus. Kafafan yada labaran dai sun ce masu kutsen sun so satar bayanai a ma'aikatun harkokin waje da tsaro a Jamus.