1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Shirin daukar matakan dakile Covid-19 a karo na biyu

Binta Aliyu Zurmi
July 16, 2020

Bisa ga wata yarjejeniya tsakanin gwamnatin tarayya da na jihohi a Jamus, akwai shirin daukar tsauraran matakai na hana zirga-zirga domin dakile yaduwar cutar Covid 19 saboda fargabar barkewar cutar a karo na biyu.

https://p.dw.com/p/3fPrX
Deutschland Bundeskanzlerin Angela Merkel
Hoto: picture-alliance/AP Photo/P. Kneffel

Daga cikin sabbin dokokin, za a hana shiga da fice daga duk yankunan da aka sami karuwar cutar. Ana sa ran cimma matsayan karshe kan wannan mataki a wannan rana ta Alhamis.

Jamus da ta sami saukin annobar idan an kwatantata da sauran makwabtanta, ba ta son cutar tai mata zuwan bazata a wannan karon wanda hakan ya sa suka yanke shawarar daukan matakai tun da wuri.

Shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel a ranar talatar da ta gabata ta nuna goyon bayanta ga wannan mataki.