Bala'i
Hari da wuka a Jamus ya halaka mutane biyu
October 18, 2022Talla
Mutane biyu sun mutu kana na uku ya samu raunika sakamakon hari da wuka a yankin kudu maso yammacin Jamus. 'Yan sanda sun kama maharin bayan bude masa wuta mai shekaru 25 dan kasar Somaliya a garin Ludwigshafen.
A kasar ta Jamus ana samu hare-hare masu nasaba da matsanancin ra'ayi da kuma masu matsalar kwakwalwa, amma zuwa yanzu 'yan sanda ba su bayyana dalilin harin da aka kai a wannan Talata ba.